Boss Bature Takun Karshe Complete Hausa Novels

💋Boss Bature💋*



Join this link to follow my tiktok acct👇

https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1



قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*

*Father of soldiers*

*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*


⭐💫⭐💫⭐💫⭐💫⭐💫⭐
*MACE MAI GYARA KANTA BATA BORANCI*💃🏻💃🏻

Sis ko kinsan illar rama ajikin mace in tayi yawa ??? Rama Sam batayi ba mijinki kullum yana iya kokarinshi akanki amma da yawa mutane sai suyi maki kallon kina cikin matsala ne saboda ramar da kikeyi , sannan zaki zquna a abushe bawata mat'aba ajikinki 🤣🤣 wannan yasa nazo maki da maganin kiba mai inganci hajiya yadda zaki ciko sosai ki murje abunki bawai kiba mai yawa ba aa zaki ciko dai kikoma yar dai dai misali ke ba katuwaba ke ba ramamma ba yadda kema zakiji dadin yin kwalliyar da zataja hankalin mijinki agareki😉😉 mmn Yusuf fa ta shirya tsaf domin gwangwaje Ku da zafafan kayanta uwayen gida da Amare👍🏼👍🏼👍🏼👍🏼07069711327


*Boss Bature ✍️*


Innanillahi wa inna ilaihi raji un abunda take fitowa daga bakin jahad baby Junaid tana gama fadin haka tayanke jiki tafadi asume lokaci kankani mutane suka cika wajan kowa yarazana daganin abunda yafaru dankuwa motar Junaid ta markade badama asamu mutum me rai acikinta sai wani mutumne yafara tinanin akira police

Boss bature

Abankaran aunty babba kuwa fitowarta kenan daga wanka bataga abra ba saitafara tinanin ina tashiga 
To yansaka ido Nima jiranakeyi tafara nakaranta amma nasan na nishadantar daku ina bukatar addu arku my my friends takuce mommy hajara😂😂😂😂😂😂😂😂😂😂😂😂😂🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣Dan Allah karku dakeni
 JUNHAD*

Saukowa sukeyi downstairs hannunsu ruƙe acikin na Juna,
   "Tun ɗazu nake kiran Layin Rishi,Amma bata ɗagawa,I don't know why,nashiga damuwa,"jahad ce tayi maganar,fuskarta da ɗan damuwa,
  Junaid yace"may be tana busy ne,amma ki bari zuwa anjima sai mu jaraba kiranta,may be ta ɗaga wayar,"
  Cikin palour suka saukko,hosana na ganinsu ta miƙe tana sakar masu murmushi,
  Ba ƙaramin burgeta su kayi ba yarfa hannu ta shiga yi tana faɗin"Wow,jahad junaid kunyi kyau kamar sabbin kuɗin da Central bank suka fitar,"gaba ɗaya suka fashe da dariya,
   camera ta shiga,tare da ɗaukarsu hotuna da wayarta,kafin suka wuce tare da barin palourn,komawa hosana tayi saman sofa ɗin tana jiran dawowar Ya Omar,

Wurin motarshi suka nufa,da kanshi ya buɗewa jahad mota,ta shiga,kafin ya zagaya other side ɗin,ya buɗe ma kanshi motar ya shiga,
juyawa ta ɗan yi tare da kallon fuskarshi,Murmushi ta samu akan fuskarshi,
  Cikin sanyin murya tace"Babyna,"
  "Na'am" ya amsa mata tare da wurga idanuwanshi akanta,
  Kashe mashi ido ɗaya tayi kafin tace"Junaid,I love u so much,I can sacrifice my life for u,"
  Ƙayataccen murmushi ya saki,tare da cewa"Me too,",yana ƙoƙarin tashin motar yaji gabanshi yayi wani irin mugun bugu mai sautin gaske ji kake daraaam!har razana sai da yayi,lokaci guda yanayin fuskarshi ya canza,ganin ya kasa tashin motar yasa jahad,cewa"Babyna,Lafiya naga yanayinka ya canza"?
  Ashagwa6e yace"jahad,faduwar gaba nake ji,kamar wani mummunan abu zai faru dani,haka nake ji,"muryarshi a kasalance yayi maganar,
  Cikin sanyin murya tace"In sha Allah babu abunda zai faru da kai babyna,idan har fitar nan da zamuyi bata kwanta maka arai ba,ni inaga kawai mu koma gida..."tunkan ta ƙarasa maganar,yace"a'a,Bazamu fasa ba,na sa rai sosai akan fitar nan,"
  Jinjina kai jahad ta ɗan yi tare da zura hannu cikin ƴar purse ɗinta dake ajiye saman laps ɗinta,Phone ɗinta ta curo tare da buɗeta,adai adai lokacin app ɗin da take amfani dashi na V muslim wurin yin azkhar yayi mata alert na cewa time ɗin yin evening azkhar yayi,
  Juyawa ta ɗanyi tare da kallon junaid,wanda jikinshi duk yayi sanyi,
  "Babyna,yakamata muyi azhkar kafin mu fita daga gidan nan,"
   Ashagwa6e yace"jahad ni ban iyaba,bansan ya zanyi ba,"
  Moving tayi close to him tare da nuna mashi screen ɗin wayarta"kalli ka gani,App ne nake using dashi yana da matuƙar amfani,kuma yana taimaka mun wurin tunasar dani lokuttan yin sallah da kuma yin azhkar,koda ace baka iya ba,zaka iya yi yayin da kake kallo kana karantawa acikin zuciyarka,"
Murmushi ya ɗan saki kafin yace"Its ok my juliet,mu fara atare,"
  Nan suka shiga yin azkhar ɗin acikin zuciyarsu,har suka kammala,tukunna 
yaja motar da gudu ya nufi hanyar fita daga gate ɗin gidan,a bakin gate ɗin ma sai da jahad ta ƙara tunasar dashi akan yin addu'ar fita daga gida kuma atare suka furta"Bismillah,Tawakkaltu Alallah,wala haula wala ƙuwwata illa billah",

Fitar motarsu keda wuya,Sai ga motarsu Marshal Omar na shigowa cikin gidan,Hatta gifcinsu sai da marshal Omar ya gani,
  "Yalla6ai,kamar motar junaid ce ta wuce yanzun nan"major ne yayi maganar,
Omar dake zaune a back seat na motar yace"I think so,"
  "Amma yalla6ai,kada kace nayi shisshigi,ni dai aganina bai kamata junaid na fita yawo shi kaɗai ba without security guards atare dashi,duk da munsan Allah ke tsare bayinsa,"
shiru Marshal ya ɗan yi yana nazarin wani abu kafin yace"Ni kaina na jima ina tunanin hakan,last time har maganar mu kayi da Rafayet,amma daga baya kowa ya share maganar,"
Major yace"gaskiya yakamata aduba,saboda yaron yana da farin jini sosai,kuma kowa yasan irin son da kuke yi mashi,duk wani mai hakon family ɗinku zai iya biyowa ta wurinshi ne"_
Jin wannan maganar ta Major,yasa hankalin Omar ya tashi,saboda an sha faɗa masu cewa junaid,Shi ne lagwansu,Duk wani wanda zai kawo masu hari acikin masu son ganin bayansu,dole sai an ƙuntatawa junaid sannan za'a ta6a zuciyoyinsu,

  "Major thank u so much for ur advise,and in sha Allah zanyi wani abu akai,'

Bayan Major yayi parking ɗin motar,Ya buɗe ya fito tare da zagayawa ya buɗewa Marshal,Saukowa marshal yayi,ya nufi cikin gidan,lokacin da ya shiga babu kowa a main palour ɗin,Bedroom ɗinshi ya wuce,Shaf shaf ya cire kakin dake ajikinshi,Ya wuce cikin toilet,after some minutes ya fito daga cikin toilet ɗin,sanye da short a jikinshi,Agajiye yake ga wani irin bacci da yake ji,Saman gadonshi ya haye,in a short time bacci ya ɗauke shi,


A hankali Hosana ta turo ƙopar dakin nashi,tun tana kabbara sallar la'asar ta jiyo shigowar mota cikin gidan,jiki na rawa ta sallame bayan ta gama sallar ta fito,saboda tana da tabbacin cewar Ya Omar ɗinta ne ya dawo,murmushi ta saki ganinshi kwance da gajeran wando ajikinshi,ya baje sai faman sharar bacci yake yi,lalla6awa tayi cikin sanɗa ta haye saman gadon,saman jikinshi ta hau,har zuwa saitin fuskarshi,ta ƙura mashi ido tana kallon kyakkyawar fuskarshi,bata da da burin da ya wuce ta takura mashi arayuwarta,
   "Bari nagani,idan na toshe mashi hancinshi da bakinshi,ta ina zai yi numfashin,"
  Hannu tasa,cike da mugunta,ta toshe mashi hancinshi da bakinshi,ta danne su da tafin hannunta,aikuwa nan take numfashinshi ya soma tattokarewa,A razane ya farka lokaci guda,ya rarumeta batare da ya ankara ba,yayi wurgi da ita,da iya ƙarfinshi na ƙarshe,kai tsaye hosana ta faɗi ƙasan gadon yaraf!kanta ya bugu sosai,fashewa tayi da matsanancin kuka tana fadin"Wayyo Allah na,Ya Omar ka kashe ni wllh,"
  Tunda yaji muryarta,ranshi ya 6aci sosai,saboda ita taja har yayi mata hakan,ko kwanakin baya ta ta6a yi mashi irin hakan har yayi wurgi da ita,miƙewa yayi daga zaune tare da kai idanuwanshi wurin da take yashe a ƙasa tana kuka,
  Da wata irin kasalalliyar murya yace"Why Hosana!why!"?
   Sai faman shessheƙar kuka take yi,tama gaza ɗagowa da kanta,
  Guntun tsoki yaja,kafin ya sauko saman floor ɗin,hannu yasa ya janyota jikinshi ya rungumeta a saman faffaɗan ƙirjinshi,yana ɗan bubbuga bayanta,Cikin lallashi yace"Am so sorry My Hosana,duk laifinki ne,meyasa kike son takuramin ne?
  Cikin shesshekar tace"ya..ya..Omar,nifa wasa nake yi maka fa..."
  "Haka ake yin wasa a garinku?You are trying to kill me,and u are saying that it was a joke!"
   "Ya Omar,nima fa a wani Chinese film ne nagani,Na jakican,shi ne na kwaikwaya,"
   A ruɗe ya ɗago da kanta daga saman ƙirjinshi yace"Ke!ashe dagaske baki da hankali,saboda kawai kin kalli film kinga anyi haka sai kice nima zaki jaraba akaina?angaya maki cewa abunda ke cikin film dagaske ne?Su idan sunyi sun rayu,to ni idan kika yi mun kashe ni zakiyi,"
  Runtse idanuwanta tayi ganin yadda yake ta surfa mata faɗa,
  Tsagaitawa tayi da yin kukan da take yi"Am sorry Ya Omar bazan ƙara ba,"
  Harara ya ɗan watsa mata"kinfi kowa iya bada haƙuri,idan kikayi laifi kamar matar aure ta gari,"
  Murguɗa mashi baki tayi,lokaci guda ya samu kanshi cikin wani irin yanayi,zuba mata ido yayi yana kallon dress ɗin dake ajikinta,Jeans da t shirt sunyi matuƙar bin shape ɗin jikinta,jin yayi tsit yasa ta ɗan buɗe idanuwanta,ganin ya zuba mata ido ko ƙyaftawa baiyi ba,yasata fara tunanin kome yake kallo ajikinta,Ganin yana kallon ƙirjinta yasa tace"Ya Omar sun ƙara girma ko"?
Waro ido ya ɗan yi tare da cewa"Mekenan?"
Hannu tasa tana nuna mashi breasts ɗinta,
  "Ya salam,"ya furta hakan tare da ɗan rufe idanuwanshi yace"nifa,basu nake kallo ba,kayan jikinki ne suka burgeni,sunyi maki kyau sosai,"ya ƙarasa maganar tare da miƙewa tsaye yana kallonta,
   "Idan kana jin yunwa in kawo maka abinci"?tayi tambayar tana kallonshi,
   ɗaga mata kai yayi alamar eh,sannan yace"pls,inaso in ɗan kwanta in huta kinga baccin bai ishe ni ba,idan kika kawo mun Lunch ɗin,ki ajiyemun shi saina farka zanci,"
  Amsa mashi tayi da toh,kafin ta miƙe da sauri da sauri ta fuce daga ɗakin,saman gadon ya koma ya kwanta,bakomai bane ya faɗo mashi aranshi ba,fa ce maganar da suka yi da Major dangane da Junaid,hakanan ya dinga jin kamar yayi kuskuren barinshi ya wuce da motarshi,dama ya sani tun a time ɗin yasa security sun bi Bayan Motarshi...........


*Boss Bature*

Ƙarar shigowar Message,da ta ji ne yasa takai hannu tare da ɗaukar wayarta dake ajiye agaban mirror,yayin da take zaune asaman kujerar gabanshi,tana yin makeup,janyo wayar tayi tana karanta message ɗin daya bayyana akan screen ɗin wayar,
   _Abra,inason magana dake,amma bana so kowa ya sani,koda Aunty Laila ce_
  Mamaki ne ya kamata ganin anyi mata saƙo da new number,kowaye wannan,ɗaukar wayar tayi tare da miƙewa tsaye,a lokacin Aunty babba na cikin toilet tana yin wanka,

Arab gown ce ajikinta,pink colour abunka ga fara tass,ba ƙaramin kyau tayi mata ba,fitowa tayi daga cikin bedroom ɗin nasu,ta miƙi hanya kamar zata fita daga corridor ɗin,Sai da ta bada tazara sosai,Sannan ta dannama numbar kira,tana fara ringing aka ɗaga,
  Tun kafin tayi sallama,taji muryar hayaam tace"ABRAH"!tun daga kan yadda ta kira sunanta yasa gabanta ya faɗi rass,
   "Aunty hayaam kece"?
Bata amsa mata ba,sae ma fashewa da tayi da kuka mai sautin gaske,hakan ya ƙara ɗagawa Abra hankali,a ruɗe ta shiga faɗin"Aunty hayaam meya faru dake ne?meyasa kike kuka?dan Allah kiyi mun bayani,"

On the other hand,Hayaam ta miƙa ma Amani wayar tare da cewa"kiyi mata bayani,"
  Gyaran murya Amani tayi tare da ambaton sunan Abra,
  Duk sunbi sun ɗaga mata hankali,muryarta har kerma takeyi wurin cewa"Dan Allah kuyi mun bayani,kun sanyani acikin duhu,"
  "Abrah!ki natsu ki saurareni,"jinjina kai abra ta shiga yi tana fadin"ina sauraranki Aunty Amani,meya faru ne naji Aunty hayaam tana kuka,
  Amani bata 6oye mata komai ba,game da abunda ya faru da hayaam da kuma guduwar Aunty babba daga asibitin,da kuma wasikar da ta bar mata,wasu irin zafafan hawaye ne suka soma gangarowa akan fuskar Abra,hankalinta a matuƙar tashe tace"Nashiga uku!kenan nima wata rana idan ƙaddara ta same ni,Aunty laila zata iya guduwa ta barni?
  Amani tace"ƙwarai kuwa!saboda bata da Imani kuma bata da tausayi,karki so kiga yadda na samu hayaam a asibitin nan a wulakance,kamar wadda tayi hatsarin mota amma a haka laila tabarta,saboda bata da amfanin da zata yi mata,To kema muddin kika kuskura kika bita wurin bokan nan rayuwarki ta faɗa halaka,Kuma wlh da zarar amfaninki ya ƙare a wurinta shikenan kin zama Waste product!Zata yi watsi dake ne,"jin wannan maganar yasa Abra ta fashe da matsanancin kuka,wani irin tsoro ne ya kamata,don Aunty babba ta zama abun tsoro a wurinta,ta girgiza da jin rashin imaninta,
Da gangan Amani ta dinga tunzura abra don ta tsoratar da ita akan karta goyi bayan Aunty babba suje wurin bokannan,
  "Abra!ina ƙara jan kunnanki,karki kuskura ki bi ta,Kiji tsoron Allah,ki tuna cewa wata rana zaki koma gare shi,kada kiyi silar da za'a cutar da rayuwar wasu,Aunty laila bata da Imani,tanaso ta jefa rayuwarku cikin haɗari ne,kuma tana yin amfani da ku ne don ta cimma burinta,kuma da zarar amfanin ku ya ƙare a wurinta,zata yi watsi daku ne,ta kama gabanta,Ga hayaam nan dai yanzu ta gane kuskuren da tayi,tana mai dana sanin abunda ta aikata,"
  Amani nakai ƙarshen maganarta,ta miƙa ma hayaam wayan"kiyi mata magana,"
  Kar6ar wayar hayaam tayi tare da karata a kunnanta,Kukan da Abra keyi har cikin zuciyarta,dama tasan dole taji raɗaɗin acikin zuciyarta,ɗan uwa ba wasa ba,
  Cikin Sanyin murya tace"Abra,baki ga yadda na koma ba,bani da wani abu daya rage na ƴa mace a jikina,komai ya lalace,Yanzu ma bana jin kaina amatsayin mace,"
  Wani sabon kukan Abra ta ƙara fashewa dashi,cikin shessheƙa tace"Aunty hayaam wlh bazan bi ta ba,sai dai taje ita kaɗai,Ashe ba son mu take yi ba,bata ɗauke mu abakin komai ba,Amfani kawai take yi damu don ta cimma burinta,Ni wlh bansani ba Aunty hayaam,harfa tambayarta nayi ina kike amma tace mun wai batasan inda kika tafi ba,kinacan kina yawon gantali,Ashe kina gadon asibiti rai hannun Allah,yanzu haka fa da nake yin maganar nan,tun jiya muka iso Enugu da ita,Yanzu haka ma shirin zuwa wurin bokan muke yi,
  Hayaam tace"Abra,ki natsu ki saurare ni,kada ki bari tasan da shirinki naƙin binta wurin boka,saboda bata da imani tana iya kasheki,in kika 6ata mata rai,Abunda nake so dake shi ne,Duk wani kuɗi dake a wurinta,ki tattarasu gaba ɗaya ki sanyo su acikin jakarki,muguwar rabi da kwata na kuɗin dake a hannunta nawa ne,amma saboda tsabar rashin Imani ta kwashe hada nawa ta gudu dasu,"
  Jinjina kai Abra tayi yayin da take share hawayenta,
  "Aunty hayaam,yanzu tana acikin toilet,bari nayi sauri na tattara kayana,in biyo mota in dawo nan,"
  Hayaam tace"Yawwa,kiyi sauri kada fa kiyi kuskuren da zai sa ta gane cewa guduwa zakiyi ki barta,".  
  "In sha Allah bazan bari ba,"
.daga haka su kayi sallama,

Ajiyar zuciya hayaam ta sauke tare da kallon Amani dake zaune gefen gadon,tace"Har hankalina ya kwanta,So nake Aunty laila ta ɗanɗani kuɗarta,taji irin raɗaɗin dana ji acikin zuciyata,
  Murmushi Amani tasaki,tare da cewa"Nafi ki jin daɗi Hayaam,A shirye nake dana taimaka muku wurin ganin kun gyara rayuwarku,"acikin ranta kuma tace"Ita kuma waccen bijimar,Sai nasa ta tsani kanta,duk wani makusancinta saina kwace shi ya dawo a ƙarkashin ikona,So nake ta gane kuskuran da ta aikata arayuwarta,"

A 6angaren abra kuwa,tun bayan da suka kammala yin wayar,jiki na rawa ta koma Room ɗin nasu,A hankali ta tura ƙopar ta fara leƙawa ciki,don taga ko ta fito daga wankan,Ajiyar zuciya ta sauke,ganin bata fito ba,da sauri ta faɗa cikin ɗakin,Jikinta sai kerma yake yi,asaman bedside drawer,ta samu jakar Aunty babba,hannu tasa ta ɗauki handbag ɗin,tare da zagayawa ta Other side ɗin ta ɗauko ƴar purse ɗinta,saboda tsabar sauri jin Aunty babba na motsi kamar zata fito daga cikin toilet ɗin,aikuwa a gigice ta buɗe ƙopar ɗakin ta fuce,da gudun gaske,mutanen dake kai komo a cikin hotel ɗin sai kallonta sukaye,wasu kallon burgewa suke yi mata saboda rigar jikinta,ba ƙaramin kyau tayi mata ba,gashi bata sanya mayafi akanta ba,ƙafafunta ko takalma babu,

Hankalinta bai kwanta ba,har sai da ta fito daga cikin hotel ɗin,gudu gudu sauri sauri ta miƙi hanya tana tafiya tana waiwayon bayanta kada ace Aunty laila ta biyota,Masu motoci sai parking sukeyi agabanta suna yi mata tayin shiga motarsu,amma taƙi sauraron kowa saboda gudun kada wani ya cutar da rayuwarta,kamar yadda aka yiwa Hayaam,baiwar Allah ta tsorata sosai,gashi babu wanda ta sani a garin,haka bata san ko ina ba,ba ƙaramin galabaita tayi ba,

    *Koya Abra zata ƙare?Shin ina Aunty Babba dake a cikin toilet tana wanka?Batasan an yashe ta ba*

*Boss Bature*

   ❤🤍❤

Kano state

Wuraren ƙarfe 6 na marece,Slowly motocin Sgr suka shiga cikin unguwar batare da jiniya ba,saboda patient ɗinsu da suka ɗaukko,a back seat na motar Abusufyan suka kwantar da ita,Abusufyan shi ne ke driving ɗin motar,fuskarnan tashi a washe,kamar wanda aka yima Albishiri da Gidan Aljanna,Sehrish na agefenshi sae faman sakin murmushi take yi tana waiwayawa,bakinta yaƙi rufuwa,a ƙagare take dasu ƙarasa gidan,ko ta samu ta kira sauran ƴan uwa ta sanar dasu cewa An samo Oummansu,

Bayan motar su Abusufyan Motar dake ɗauke da Baban Sadeeq ce,tare da Maman Sadeeq,ɗaya daga cikin motocin Sgr ne,wanda wani soja ke driving ɗinsu,
Mamaki yaƙi barinsu,musamman Maman sadeeq,abun ya ɗaure mata kai har tagaza rufe bakinta,
Kasa kasa tace "Baban Sadeeq kaga wani iko na Ubangiji"?
  Murmushi Baban sadeeq yayi tare da kallonta yace"dama ae naji ma ina sanar dake cewa,Allah yana tare dasu,kuma shi zai kula da abunshi,Yau nasan kin shaida maganata,"
Murmushi ta saki tunawa da wannan kalami na Baban sadeeq,a duk lokacin da ta rufe shi da faɗa kan cewa sunƙi ɗaukar mataki akan Ya sayyadi,yana ta cutar da bayin Allah,an zuba mashi,sai babban sadeeq yace mata"Bazan iya tunkarar mutumin nan ba,Mutumin da kana ja mashi ayar ƙur'ani yana fassara maka?taya zan iya tunkararshi?in dai akan yara ne Allah yana tare dasu,Kuma shi zai kula da abunshi,"
  "Amma gaskiya Baban sadeeq,nayi matuƙar mamaki,har yanzu fa ji nake yi kamar mafarki nakeyi wlh,wai yanzu waɗannan danginsu rishi ne?bayin Allah,wlh na tayasu murna sosai,"
  Baban sadeeq yace"Ni ji nake kamar nafi kowa farin cikin wannan ranar wlh,Alƙawarin dana ɗaukarwa kaina,Ya cika yau ga abu ga Ƴa'ƴanta,ga kuma danginsu,Godiya ta tabbata ga Allah subhanahu wata'ala,"

A bayan motarsu dasu Baban sadeeq suka,Motar dake biye da tasu,nurse ce ɗaya tare da Dr,An zo dasu ne don a nuna masu gidan,Saboda sune zasu ci gaba da zuwa suna duba lafiyarta,security guards sun sanya motocinsu a tsakiya,gaba da baya duk motocin Soldiers ɗinne,Sgr baisamu ya biyo bayansu ba,Sun wuce Hotel shi da Armstrong,

A parking space suka tsayar da motocin nasu,fitowa Abusufyan yayi tare da zagayawa ya buɗe gidan baya,Hannu yasa ya kinkimo abu,tare da azata asaman kafaɗarshi,gaba ɗaya suka kama hanyar shiga cikin falon gidan,tun kafin su shiga ciki sehrish ta fara ganin canji alamun kamar anyi gyara acikin gidan,shi kanshi Abusufyan yayi noticing hakan,

Main palour ɗin suka shiga,Nan fa suka sha mamakin ganin an canza Sofa set ɗin falon izuwa sababbi,Hatta ƙasan falon wani jigunannan carpet ne aka shimfiɗa ya mamaye ko'ina,ga wani irin sanyi na A.c dake ratsa ko'ina cikinshi,Abun ya ɗaure masu kai,
   "Abba kodai munyi mistake ne"?Sehrish ce tayi maganar,
  "Ba kuskure mu kayi ba sehrish,ni kaina nayi mamaki,daga gani aikin Sgr ne,Shi ya sanya aka gyara gidan,dama ina ta fargabar awani wuri zamu aje Oummanku"yayi maganar,a yayin da suke tunkarar Bedroom ɗin abu,ciki ya shiga da ita,nan ma an sanya A.c ɗin,daga gani duka gidan aka gyara,hatta furniture ɗin duk an canzasu,Naira tayi aiki daga safe zuwa maraice gidan ya koma tamkar na amarya,amaryar ma yar masu fada aji,a hankali ya kwantar da ita saman gadon,wuri ya samu gefen gadon ya zauna yana ƙare mata kallo cikin zuciyarshi kam hamdala yake tayi,
  Sehrish dake tsaye tana kallon fuskar Oumman tasu,sae faman sakin murmushi takeyi,ji take kamar ta faɗa jikinta ta rungumeta sosai,'
  Sehrish ki zauna gefenta,bari na fita wurinsu Baban sadeeq,mun barsu a palour,"yayi maganar tare da miƙewa ya fuce daga ɗakin,
  Wuri Sehrish ta samu daga gefen gadon ta zauna,tana kallonta,
  "Allah ya baki lafiya Oummanmu,Nasan zakiyi farin ciki sosai,idan kika ga yadda ƴan ukunki suka koma,Ashe da rabon mukai wannan lokacin araye,mu dukkanmu"?hawaye ne suka soma saukowa daga saman fuskarta,kwantar da kanta tayi daga gefen Oumman,ta sanya hannunta tare da ruƙo nata,

Lokacin da Abusufyan ya koma palourn,A zaune ya samu Malam Nura tare da Maman sadeeq saman 3 seater,Nurse ɗin kuwa tana zaune saman 2 seater ita da Doctor,

After few minutes da shigarshi palourn,Sae ga wani Soja ya shigo hannunshi ruke da manya manyan ledoji na restaurant,A bayanshi kuma wani sojan ne hannunshi ruke da Katan katan na lemunsha,Saboda tsabar farin ciki,bakin Abusufyan yaƙi rufuwa,dama tunanin da yake yi kenan,gashi sun shigo da baƙi kowa ya kwaso yunwa gidan kuma ba wani abunsha,Balle abinci,
   Ƙarasowa ciki sukayi tare da ajiye kayan a tsakiyar palourn,
   Atare suka haɗa baki wurin cewa"Sgr ne,yace a shigo maku dashi,zaizo anjima,"
  Murmushi Abusufyan ya ɗan saki tare da cewa"Okey,mun gode sosai,Allah ya kawo shi lafiya,"
Juyawa su kayi atare suka bar ɗakin,

  Sehrish ya kira,ta ɗauki ledojin takaisu kitchen,acan ta haɗo masu kayan abincin A cikin warmers ta jerasu a saman tray,Saman dining table ta jera masu su tare da drinks,Gaba ɗaya nan suka harhadu,dama kowa ya kwaso yunwa,don sun jima a asibitin nan,Nan fa kowa ya shiga ɗurama cikinshi abinci,bayan sun ci sun ƙoshi,daga bisani,wuraren sallar magrib,Nurse ɗin tare da doctor su kayi masu sallama,

Abusufyan ne ya ɗauko su acikin motarshi tare da Baban sadeeq saboda zasu wuce masallaci daga nan,'


Tun bayan da ta kammala sallar magrib,ta koma saman gadon Oummasu ta zauna tana kallonta,a ƙagare take da ta farka duk da tasan cewa,ba a hayyacinta take ba,batasan wacece ita ba ayanzu,
  "Yakamata in sanarwa su Jahad da hosana,"tayi maganar cike da zumuɗi ta dauki wayarta dake ajiye gefenta,
  Contacts ta shiga,tare da lalubo numbar jahad ta danna mata kira,Kusan sau uku tana ringing ba'a ɗaga ba,hakan yasa ta tura mata text message,
   Layin hosana,ta kira itama wayar bata a kusa da ita,tayi ringing harta katse ba'a ɗaga ba,
  Yanke shawarar kiran junaid tayi,cikin rashin sa'a ta samu wayarshi a kashe,
  Tur6une fuska tayi ranta a 6ace,taso ace itace zata fara yi masu albishirin ganin Oummansu,Amma duk sun ƙi ɗaga kiran wayarta,
  Yunƙurawa ta ɗan yi saitin fuskar Oummansu,ta ɗauketa photo da camera ɗin wayarta,kusan hoto uku tayi mata,
ta whatsapp ta tura masu hotunanta,'


Motsin mutane taji acikin palourn,ranta ya bata cewa Su Baban sadeeq ne suka dawo,bata leƙa ba,kwanciya tayi a gefen oummantasu,

Su biyu suka shigo cikin palourn,zama sukayi saman sofas ɗin suna fuskantar juna,Abusufyan yace"Bamu da wasu kalmomi da zamu iya amfani dasu wurin gode maku,kunyi matuƙar yin ƙoƙari,kun kula da rayuwar abu,tamkar ƴar cikinku,kun damu da ita sosai,Allah ne kaɗai zai iya sakamaku,"
  Baban sadeeq yace"duk yiwa kaine,idan ka taimaki rayuwar wani kaima Allah sai ya taimaki ta ka,Naji daɗi sosai,kuma nayi matuƙar farin ciki,daya kasance kaine Mijin Zainab duk da an shiga tsakaninku,kuma mahaifinsu sehrish!hankalina ya kwanta sosai,Abu zata rayu atare da mijinta ga kuma ƴa'ƴanta,uwa uba kuma ga dangin mijinta,Allahu Akhbar,najiye mata daɗi,ƙarshen wahalarta yazo da yardar Allah,"
  Murmushi Abusufyan yayi tare da cewa"Amma malam,Ya maganar sayyadi ne!?ko kuna da labarinshi"?
  Shiru Malam nura ya ɗanyi na wani lokaci yana tunani kafin yace"Ae Sayyadi tun ranar da aka nemi abu aka rasa,tun daga ranar bamu ƙara sanyashi a idanuwanmu ba,gidan ma a garƙame muka same shi da ƙaton ƙwaɗo,". 
  dakatawa yayi da yin maganar,
Hakan yasa Abusufyan cewa"dama nasan bazai tsaya ba,guduwa zai yi,"
  Girgiza kai Baban sadeeq ya ɗan yi tare da cewa"A'a,bana tunanin ya gudu,Munafukin duk inda yake yana acikin garin nan!yanzu haka ba mamaki yasan da zuwanku!ae ba ƙaramin shu'umin mutun bane,"
  "Amma taya akai kasan cewa,yana acikin garin nan?ko kun ƙara haɗuwa dashi ne"?acewar Abusufyan,
  Baban sadeeq yace"ƙwarai kuwa!Kama tuna min!ae can shekarun baya lokacin da aka nemi abu aka rasata,fitsararran ya tako da waɗannan ƙafafuwan nashi masu kama dana zabbi har ƙopar gidana,
  Lokacin na dawo daga sallar asuba,na shiga da mashin cikin gida,nadawo zan rufe ƙopa kenan ina ƙokarin rufewa,Naji an banko mun ƙopar,A firgice na kai idanuwana wurin don inga wani taƙadirinne!aikuwa sai nayi tozali dashi,A tsaye ruƙe da qugu,nan fa nashiga faɗin A'uzubillahi minasshaiɗanir rajim,"sai cewa yayi"Ni ne shaiɗanin"?nace mashi "to ae baku da bambanci da shaiɗan,ƙahonne kawai ke babu!shin me ma yakawo ka ƙopar gidana?ko kazo ne kayi mun futsarar taka daka saba ne?sai yace mun saƙo ne yazo dashi,nace saƙo kuma?yace mun eh,yasa hannu cikin aljihun jallabiyarshi ya zaro wata ƴar doguwar takarda,ya miƙo mun tare da cewa"Saƙon Abu ne,idan mun sameta,A bata wasiƙar," jin cewa sakon na abu ne yasa na amsa,to tun daga wannan lokacin da ya haura ƙafa,ban ƙara sanya sayyadi acikin idanuwana ba,hatta makarantar islamiyyar da muke koyawa atare dashi,ya daina zuwa...."
  Lokacin da ya kai ƙarshen labarinshi,Abusufyan yace"Amma kun karanta wasiƙar"?
  Baban sadeeq yace"A'a,babu wanda ya ta6a ta,Ae amana ce,yace wasiƙar ta abu ce shiyasa bamu karantata ba,"
  A ƙagare Abusufyan yake daya ga wannan wasiƙar,
   "Yanzu wasiƙar tana ina ne"?
"Tun lokacin dai,bayan tafiyar sayyadi,dana shigo cikin gida,kaitsaye wurin Maman Sadeeq na wuce,ita nabawa ajiyar wasiƙar," 
  Ajiyar zuciya Abusufyan ya sauke,
  "Gobe,in Allah ya kaimu,sai muje gidan a ɗauko wasikar,yau dai anan zaku kwanan mana,"acewar Abusufyan,
   "Akwai yaronmu fa,mun barshi a gida,"Baban Sadeeq ne yayi maganar,
   "idan mun fita yin sallah,sae mu dawo tare dashi," acewar Abusufyan
  Suna cikin tattaunawar nan aka kira sallar isha'e,atare suka fita yin salla daga can zasu wuce gidan,Su ɗaukko Sadeeq,

Fitowa Sehrish tayi daga Bedroom ɗin Oummansu,wuraren ƙarfe 8:30 na dare,a palour ta samu Maman sadeeq zaune,jikinta sanye da hijabi,
  Tana ganin Sehrish ta mike,tare da tunkararta,
  "Rishi,zonan mana,baki bani labarin ya kuka ƙare ba,bayan kun bar nan"tayi maganar tare da ruƙo hannunta,saman 3 seater suka zauna,
  Nan fa Sehrish ta shiga bata labarin rayuwarsu,tun daga lokacin da suka koma katsina har ƙarshe,jikin Maman Sadeeq ba ƙaramin sanyi yayi ba,jin irin wahalar da suka sha,ta wani 6angaren kuma ba ƙaramin farin ciki tayi ba,  

sun jima suna firar yaushe rabo,kafin suyi sallama kowa ya wuce ɗaki,don ba ƙaramar gajiya suka kwaso ba,

Koda Sehrish ta koma ɗaya daga cikin bedrooms ɗinsu da aka gyara masu,wanda ke a upstairs,toilet ta shiga don ta watsa ruwa ajikinta,kafin ta kwanta,Maman sadeeq kuma a downstairs ta zauna,ɗakunan su Dr haris a lokacin baya,
   fitowa tayi daga cikin toilet,jikinta sanye da undi ta ja shi har saman kirjinta,ƙarasawa tayi gaban gadon,inda ta ajiye kayan baccin da ta dauko don ta sa,tare da phone ɗinta,
  Tana ƙoƙarin kai hannu ta ɗauki wayar,Ta jiyo sautin dirar mota acikin gidan,
  "Su Daddy sun dawo kenan"tayi maganar tare da ɗaukar wayar,Har lokacin fuskarta ɗauke da murmushi,bakinta fa ya ƙi rufuwa tunda aka samu Oummansu,babban burinta yanzu bai wuci Oummansu ta dawo cikin hayyacinta ba,waƙa ta kunna ta ƙure Volume,Nan fa ta shiga yin rawa,kamar wata zautacciya,juyi ta dinga yi,iska na kaɗa gashin kanta,duk cikin farin cikin ne,yaushe rabon da tayi dancing irin haka harta manta,dama can ita ba ma'abociyar yin rawa bace,duk da tana son yin rawar,yanayin rayuwane yasa bata samu wannan damar ba,a hankali ta soma bin wakar abakinta,
 _rawa da girgiza zanyi gabanka,in jujjuya,zanyi maka albishir kayi dace da mai tarbiyya,sannan zan zame maka farin ciki na nan gidan duniya,Nafi kowa saninka acikin abunsha kafi son coffee_
  Bata ƙarasa baitin ba,ta tsaya cak sakamakon mutun da ta hango tsaye ta cikin mirror,ya goya hannayensa asaman wide chest ɗinshi,gabanta ne ya faɗi rass,lokaci guda ta shiga taitayinta,duk tabi ta kame kanta kamar wata mara gaskiya,

Bakowa bane fa ce Sgr,still dress ɗin ɗazu ne ajikinshi,tun lokacin da ta fara rawar yazo ɗakin,kuma ta hanyar kiɗan wakar da ta kunna ne yasa ya gane cewa akwai mutun a ɗakin,dama kuma ita yake nema saboda ya tayata Murnar ganin mahaifiyarta,

tsayawa su kayi suna kallon juna ta cikin mirror,kunya duk ta rufe ta,saboda ɗan undi ɗin dake ajikinta sharara yake,gashi ko bra bata sanya ba,

Slowly ya soma takowa izuwa cikin ɗakin,da sauri Sehrish ta nufi wurin gadon tana ƙoƙarin ɗaukar Kayan sawarta,da ta ajiye asaman gadon,
  Sai dai kafin tayi wani yunƙuri tuni Sgr ya ƙaraso wurin,at same time suka kai hannu saman kayan nata gabanta ne ya faɗi rass,yayin da take kallon hannunshi da ya ruƙo rigarta,a ɗan razane ta cire hannunta tare da ɗan ja da baya tana kallonshi,
  ɗagowa yayi hannunshi ruke da kayan sawar nata yace"Me zaki yi dasu"?
 Muryarta na kerma tace"Am..um..sanyawa..zanyi,'
  Da buɗar bakinsa sai cewa ya yi"bayan na kammala abunda zanyi kenan"?
  Gabanta ne ya kuma faɗuwa,throwing ɗinsu yayi saman gadon,gadan gadan ya tunkareta,jiki na rawa ta shiga ƙoƙarin ja da baya,muryarta na rawa tace"Dan Allah babban yaya kayi haƙuri,wlh bazan ƙara tafiya ba,without ur permission nasan nayi maka laifi,"ita duk a tunaninta,yazo ne ya yanke mata hukunci,saboda zuwan da tayi kano batare da saninshi ba,
  "Am sorry Ya Rafayet.."wani irin kallo yake bin ta dashi,wani canji ya fara gani ajikinta,kaitsaye take fisgarshi,sai ƙokarin motsa lips ɗinsa yake yi don ya sanar da ita cewa,ba hukunta ta yazo yi ba,yazo ne don ya tayata murna,Amma ina,sam ya kasa furta hakan,duk zufa ta gama wanke mata fuska,har idanuwanta sun cicciko tab da kwalla,
  Hannayensa ya sanya asaman belt ɗin wandon jikinshi,Waro ido waje Sehrish tayi,hankalinta yayi mugun tashi,tsoronta kar ace bugunta zai yi,
  Fashewa tayi da matsanancin kuka,tare da aza hannunta asaman kanta,tana faɗin"Innalillahi,wayyo Allah na,"
   Da gangan Sgr yake zame belt ɗin wandonsa,duk don saboda ya ƙara ruɗar da ita,lokacin da ya ƙare zare belt ɗin daga jikin wandon ya curoshi yana nannaɗe shi a hannunshi,A matuƙar tsorace sehrish ta juya da nufin ta gudu,Da ƙarfi ya kai hannu zai ruƙo undi ɗin jikinta,aikuwa gaba daya,Ya zame undi ɗin daga jikinta ya sulale,kasa gashi bata sanya komai ba,babu pant bare bra,saboda tsabar kiɗima,fasa ƙara tayi sosai ta fashe da kuka,tare da ƙanƙame ƙirjinta da hannuwanta,bangon ɗakin ta ƙankame jikinta na kerma,
  Duk wannan budirin da akeyi babu wanda yasan meke wakana,saboda sun yi nesa da downstairs,
  Rumfa yayi mata da faffaɗan ƙirjinshi,ya lullu6eta sosai,nan take taji wata irin natsuwa tazo mata,daddaɗan ƙamshin turarenshi ne ya mamaye hancinta,lokaci guda ta nemi kukan da takeyi tarasa,
  "Ain't trying to flog u,"ya furta hakan da wata irin kasalalliyar murya,saboda tsabar rawar da jikinta keyi,har a jikinshi yake ji,
  duƙo da kanshi yayi dai dai saitin wuyanta,slowly ya manna mata kiss,har cikin zuciyarta taji wannan kiss ɗin nashi,kafin tayi wani yunƙuri,taji tafin hannunshi asaman ass ɗinta,laushin fatar wurinne ta soma fisgarshi,har ya fara shafata yana matsarta,almost 3 mins kafin ya zame hannun daga wurin,ya zagayo dasu ta front ɗinta,sosai yayi tighting ɗin ta ajikin wall ɗin kamar zai mayar da ita,cikin cikinshi,lokacin da taji hannunshi saman gabanta,gaba daya tabi ta susuce,ta shiga ƙoƙarin kufce mashi,ruƙon da yayi mata ne yasa ta kasa yin hakan,sosai ya shiga shafa wurin before ya janyo tafin hannun nashi izuwa saman ƙirjinta,duka hannunshi biyu ya sanya,duk irin girman tafin hannunshi,sai da boobs ɗinta suka cika su fam,har babu space,damƙarsu yayi sosai tare da runtse idanuwanshi saboda wani irin yanayi da ya fara tsintar kanshi aciki,muryarshi na kerma ya ambaci sunanta"Reesh.."for the first time da Sgr ya fara furta sunanta,tunda take yi mashi aiki bata ta6a jin ya ambaci sunanta ba,tamkar baima san sunanta ba,sosai ya cusa hancinshi acikin lallausar sumar kanta,batare da ya saki ƙirjin nata ba,da alama fa Sehrish suman tsaye tayi,gaba ɗaya sun shiga cikin wani irin yanayi mara misaltuwa,sautin kiɗan da sehrish ta kunna ne ya ƙara jefasu cikin wani yanayin na sha'awar son kasancewa da junansu,Taken waƙar Love Nwantiti ya shiga,baka jin komai sai sautin breathing dinsu dake fita da zafi zafinshi,yayin da heart ɗinsu ke beating very fast at same time,tamkar zata 6allo daga ƙirjinsu,Ya salaam!

*Boss Bature*

A 6angaren su Junaid kuwa,sunsha yawo shi da Jahad,wuraren 8 suka kamo hanyar zuwa gida,bacci cike da idanuwansu,driving yake yi slowly kamar baison yin tuƙin,
   Muryarshi tamkar zai yi kuka yace"Jahad,mun ci komae amman bafa musha ice cream ɗin ba"
   "Mu haƙura Junaid,hankalina ya koma kan gida,dare yayi yakamata ace tun 6 muna a gida,"
..."Jahad,nidai inaso nasha,na kuma baki,saboda shi na fito ma ni,"
  "Asthma fa gare ka,ko ka manta ne?ni bazan so abunda zai cutar mun dakai ba,"
    Tana kai ƙarshen maganar taji,ya dakatar da motar a gefen titi,
  Juyawa tayi tare da kallonshi,tun kafin ta tambayi dalili yayi saurin cewa"Ga mai ice cream can tsallaken titi,ki jira ni a mota yanzu zanje nadawo,if not wlh bazan yi driving ɗin ba,"zuba mashi ido tayi tana kallonshi,
  Ashagwa6e ya kuma cewa"kin yi shiru baki ce komai ba,
  Murmushi ta ɗan saki tare da cewa"Kada ka damu my Romeo tunda kana so,Ni zanje na siya mana ice cream ɗin,ka jira ni a mota,naga kaman bacci ma kake ji,yanzun nan zan dawo,"ta ƙarasa maganar tare da ruƙo ƴar purse ɗin ta,
  Tana ƙoƙarin fita daga motar,taji ya ruƙo rigarta,tsayawa tayi cak,hakanan ta dinga jin zuciyarta nayi mata wani irin bugu mara daɗin ji,
   Juyowa ta ɗan yi tare da kallonshi,lumshe idanuwanshi yayi tare da buɗesu,da wata irin murya tamkar bata shi ba,ya furta mata"I LOVE U SO MUCH,"
  har cikin zuciyarta,taji wannan kalamin nashi,dawowa tayi kusa dashi,tare da tallabo fuskarshi ta manna mashi kiss a gefen fuskarshi,tana ƙoƙarin janye la66anta,ya ruƙo waist ɗinta sosai,tare da haɗa bakinsu wuri guda,a susuce suka shiga kissing ɗin junansu sosai,almost 10 mins,kafin jahad ta janye jikinta daga nashi,da sauri ta buɗe murfin motar,ta fita daga cikinta,

Tsallaka titin tayi tana tafiya tana waiwayon motarsu,wurin mai ice cream ɗin taje,mutun huɗu ta samu a tsaye suna jiran ya zuba masu,hakan yasa ta ɗan tsaya tana jiran a sallamesu itama a bata nata,
  "Jahad,"Junaid ne ya kwala mata kira,daga cikin motar,da sauri ta juya tana kallonshi dayake akwai hasken Street light daya haskaka titin,
  ɗago mata hannu yayi fuskar nan tashi ɗauke da ƙayataccen murmushi,dimples ɗinshi sun lotsa sosai,
 Murmushi ta sakar mashi itama,sai faman kallon juna suke yi,
..."madam guda nawa za'a baki ne"?muryar mai siyar da ice cream ɗin ce ya katse ta,juyawa tayi tare da kallonshi tace"Guda biyu nake so,"
  Yana cikin zuba mata Corn Ice cream ɗin,ƙarar truck ta karaɗe wurin,Wata jibgegiyar mota ce,gadan dagan ta tunkari motar da junaid ke ciki,
  Adai dai lokacin mai ice cream ɗin ya sallameta,har ta biyashi kuɗin,tun kan ta juya mai ice cream ɗin nan ya furta"Innalillahi'wa'inna ilaihirraji'un!"a wani firgice jahad ta juya don taga menene ke faruwa,Gabanta ne yayi wani irin mugun bugu,A gigice ta fasa wata irin ƙara mai sautin gaske lokaci guda tayi wurgi da ice cream ɗin dake a hannunta,A zabure ta tunkari wurin da motar junaid

Comments