MIJIN BAABATA Part 2 Hot Romantic Love Hausa Novels By Aisha Jb Allhausanovels.com.ng

 ꧁꧂꧁꧂꧁꧂꧁


    MIJIN BAABATA

꧁꧂꧁꧂꧁꧂꧁



~S3X AND ROMANCE~

*Farin Jini writer's Asso..*

_Na faso Fa! Hajiya da zafi Na , Kar Young lady tabi tawaga ta! Abin na Manyan Mata Ne! ₦300 Naira 2389596965 Aisha jubreel zenith Bank, or MTN , ku Tura shedar biya ta wannan number 07079740079.. Yan Niger zaku tuntub'i Maimuna Matar Abdullahi +22780229915.._


2️⃣ Hard'e Hannuwanshi Yai a bayanshi Yana zagaye falon wani mataki ya kamata ya d'auka game da zaman takewar rayuwar Auren su in aka cigaba da tafiya a haka Tabbas Za'a haifi d'an da ba i'do, Shin Aure zai Kara don ya samu wacce zata dinga kula da al'amuranshi da 'Yarshi ko yaya? Toh inma Auren ne yasan wacce zai kwaso ya Halinta yake? Kar yaje ya auro wacce Halinta yafi na Rabi'a Kuma, A'ah to ya zanyi? D'akinshi ya nufa ya watsa ruwa tare da shafa turare a jikinshi Jallab'iya me gajeren hannu ya saka sannan ya Nufi d'akinta tana zaune tsakiyar Gadonta Cinyarta d'auke system ta sanya Siririn eys glass "Assalamu alaikum" ya fad'a tare da rufe kofar "Amin wa'alaikas Salam" ta amsa mishi batare da ta kalli inda yake ba, Zama Yayi kusa da i'ta Yana karewa d'akin kallo ganin yanda tayi kaca kaca da d'akin ga kayan data cire ma watsasu tayi  zaiyi magana tace "Yallaɓai aiki nake fa!" Shuru yay Yana nazarinta Bayan ta juya mishi bayanta Kwanciya yayi Yana tufka da warwara Kallon agogon d'akin yayi yaga Har shad'aya ta kusa "Hamm ya kamata ki ajiye abinda kike haka, domin ina bukatar Kasancewa dake, Nima a bani lokacina Haka" cike da mamaki ta juyo Bayan ta Rufe aikin "Lokacin ka ban gane ba?" Sosai yake kallonta shima mamaki ne karara a fuskanshi "Eh Hakki na zaki bani tunda kullun sai na biyo na roka!" Wani i'rin murmushin gefen baki tayi tana fad'in "Haba dai kai kuwa duk wannan gajiyan dana kwaso zaka ce wani hakki Amma baka da tausayi fa ko hutawa banyi ba kuma gobe sammako zanyi.."


"Bani da tausayi fa kikace Rabi'a? Tsakanin nida ke nake so ki fad'amin gaskiya waye mijin? Waye me Bada umarni?" Ya fad'a Yana kallonta ganin zata kwanta "Kai ma ka sani ai kaine mijin man, so what? Saina B'ata lokaci na a kanka kaga yanzun 11 Bari na d'an runtsa kafin gobe sai da safe Kuma ka sauke min labulen window na manta ban saukesu ba" tana Gama fad'ar Haka ta kwanta tare da Jan Bargo ta Rufe jikinta..


Jan bargon yayi tare da wurgi dashi "Wai meye Haka ne? Gurin aiki mutum Bai huta ba, na dawo Gida ma bazan huta bane.." kasa Karasa maganar tayi Jin yana Jan rigan jikinta "Kaga banson fitina fa ka kyale ni na huta Mana!" Cire Jallab'iya jikinshi yayi Yana Kallon Dukiyan fulaninta Jiki a kasalance ya kai hannunshi zai tab'asu yaji ta buge mishi Hannu "Karka B'ata min breast Dan kullun cikin  tattalasu nake banso su lalace"


Sake kai hannu yayi da niyar kamasu ta tureshi a jikinta da zanin Gadon ta Rufe jikinta tana tsaki "Kai baka San Yawan s3x tsufar da mace yake ba? Wannan damuwa har i'na? Haka kawai Zaka tsufar dani da yarintata a'a wallahi bazan lamunta ba" kwafa yayi Sannan ya mayar da riganshi "Haka Kika ce ko? Nagode ki jika abinki a ruwa Kisha" "Oh ho dai Kai ka sani" sauke Mata labulen window yayi Sannan yabar Mata d'akin Yana had'a hanya Allah ya gani i'ya hakuri Yana yi Amma Bata ganin Hakan   Shiga d'akin Ameerah  yayi dan yasan yanzun Haka tabar Wutan d'akin a kunne da kyar ne Kuma in ta hau gadon Sabida kullun saiya duba ta ya Gyara mata Kwanciya Yana Shiga kuwa ya ganta kwance Akan abin sallah ta takure jikinta ta kura gudun fanka Ga AC ma dake kunne


Gyara mata shimfid'an Gadon yayi Sannan ya zare Mata doguwan Himar d'in sallan data saka yalolon doguwan rigan barci ne a jikinta me shara-shara d'aurata yayi saman gadon tare da shafa fuskanta turo baki tayi tana sake Gyara kwanciyar kai fuskanshi yayi dai-dai saman nata ya d'aura lips d'inshi saman nata lumshe ido yayi Yana sauke wahalallen Numfashi wani i'rin feeling ne yake Kara bijiro mishi da  tongue d'inshi ya Fara zagaye lips d'inta dashi tsuke bakinta tayi tana motsasu cikin barci ta fara Jin ana tab'a ta, Numfashi ta sauke, 


Sannu a Hankali ya Shiga lalub'an bakinta a hannuwanshi na rasa ya Soma wasa da jikinta jan Hannun rigan yayi take i'donshi ya hango Masa 'Yan madedetan Nonuwanta da suka Fara tasawa slowly ya d'aura hannunshi wanda ke rawa samansu wani i'rin jan Numfashi yayi Yana sauke ajiyan zuciya can Kuma kaman Wanda aka farkar dashi yayi sauri barin jikinta tare da mayar Mata da riganta daya Fara zare mata "Auzubillahi minan shaid'anin rajim" abinda yace Kenan tare da barin Gadon da sauri... Zuciyar shi na tsananta Bugawa


  lullub'e Mata jiki yai tare da  kashe wutan d'akin  Sannan ya rage gudun fankan jiki a sanyaye ya

Fita tare Nufan nashi d'akin Kwanciya yayi saman gadonshi Yana juyawa shi kad'ai yasan me yake ji a K'alla in baiyi kariya ba, wata hud'u Rabon da ya had'a shimfid'a da Matarshi wacce ta bada attention d'inta gabad'aya ga aikinta tun farkon Aurensu Haka suke Amma da da yanzun ba d'ayaba tunda a da Yana samu ko baiyi komai da i'ta ba, Yana rage zafi Kuma tana kula da Al'amura Gidanta sab'anin yanzun da komai ya lalace ya dagule..


Kwata kwata Bata da lokacin shi hakama 'Yarshi bata Ƙaunar yazo inda take damuwarta Aikinta Juyi yake Yana dafe da mararshi saukowa yayi tare da nufar kichin kanwa ya jika yasha ruwan Yana komawa d'aki ya kwanta Yana sauke ajiyan zuciya sannu a Hankali yake lumshe idanuwansa har barci ya d'aukeshi Kiran Sallan assatu ya tayar dashi toilet ya nufa ya watsa ruwa Sannan ya shirya direct ya Nufi d'akin Dakta buga mata kofa Yayi Murya cike da barci ta farka "Yes!" Yana jin ta Fadi Haka yasan taji shi fita yayi ya Nufi masjid Karfe shida dai-dai ya shigo gidan d'akin Ameerah ya nufa ya tasheta dakyar ta tashi kuwa kasancewar tana da nauyin barci..


 Tura kofan d'akin Dakta Rabi'a yayi ya Shiga tana kwance tayi d'add'aya zanin Gadon da ta rufe jikinta ya koma Gefe, Lasan bakinshi yayi lokacin da idanunshi ya hasko mishi cikakkun Hips d'inta da Na shanunta Haya Gadon yayi ya Shiga shagalinshi wani i'rin murzata yake son ranshi a firgice ta farka jin abinda yake mata kiciniya suka farayi tana kokarin kwace jikinta Amma i'na ya mata Kyakkyawan riko matseta yayi sosai tare da danneta Bayan ya hau jikinta "Nida Halal d'ina a haramta min wallahi bazai Yuwu ba.."


"Dan Allah d'agani inyi sallah takwas nake on duty ta fad'a tana Shirin tureshi a jikinta d'aga Mata gira d'aya yayi "Ai haba koba duty ba? To yau na soke fitan" a sukwane ta kalleshi "Yes babu inda Zaki je" ya fad'a tare da shigar da kanshi tsakiyan kirjinta Yana sauke nishi daddagewa tayi ta tureshi a jikinta tare da sauka a Gadon tana Kallon agogon d'akin Shida da kwata, Ban d'aki ta nufa a gurguje tayi wanka da alola ta fito mikewa yayi ya bar Mata d'akin Kofan Falonsu na shigowa ya rufe tare da rik'e makullin tana idar da sallah ta shirya cikin atamfa Riga da zani siririn mayafi ta yafa a kafad'anta fitowa tayi Rike da Jakarta ta Nufi kofa tana tab'awa taji a kulle juyowa tayi tana kallonshi


"Yallaɓai...!" Dakatar da i'ta yayi ta hanyar d'aura hannunshi saman bakinshi "Wallahi rantsuwa nayi Babu inda zakije Oya maza ki Shiga kichin ki sama Mana abinda zamu ci minti talatin na dan zan sauke Ameerah a school Sannan Gidan Nan Yana bukatar gyara shara,Goge Goge Kamshi..."


"Lallai ma kuwa wato ga baiwarka har kana lissafomin wasu tarkacen aiyuka Ehh! Dan Allah bani makulli kana B'ata min lokaci domin wlh duk wannan shirmen daka lissafo ba i'yawa zanyi ba, Haka kawai ka Kora min Masu aiki sai ka zauna ka kula da gidan aii tunda naka ne" Fitowon Ameerah yasashi yin Shuru ta fito tsaf abinda cikin shigan makaranta "Good morning Abbana Good morning Maamah" Ko kallonta batayi ba, 


"Morning my daughter kin tashi lafiya?" "Kalau Abba Yunwa.." ta fad'a tana kwab'a fuska tare da rik'e ciki Kallon Rabi'atu yayi Sannan yace "kije ki Mana girki.." Wani mugun kallo ta watsawa Yar Sannan ta kalleshi Kai tsaye Tace "Bazanyi ba!" Bai ja maganar da tsawo ba ya Kama hannun Ameerah nufarta yayi zai bud'e kofan tana Shirin fita ya tunkud'eta "wallahi rantsuwa nayi Bazanyi kaffara ba, Yau kan ki Gyara min Gidana Kuma yanzun zan dawo ki tabbata kinyi abinda nace"


"Wallahi baka i'sa ba, Yallaɓai Usman ka bud'e min kofa na tafi aiki na.." tsaki yaja Sannan ya Kama hannun Ameerah suka fita...


*Maman Faruq*

Comments